31 Mayu 2026 - 19:07
Source: ABNA24
Isra’ila Na Shan Azaba A Hare-Haren Jirage Marasa Matuki Na Hizbullah

Hare-haren jirage marasa matuka na baya-bayan nan da Hizbullah ta kai a layin iyakar Kudancin Lebanon, wanda ya jawo asara ga sojojin Isra'ila, ya mayar da yanayin rikicin yankin zuwa wani sabon mataki. Yadda Hizbullah ta fara amfani da rundunarta ta jiragen mara matuki wajen ƙara matsin kai farmaki a filin daga, ya sa Isra'ila ta sake duba manufofinta na tsaron sama na yau da kullun

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: Kara tsamarin yaki a kan iyakar Isra'ila da Lebanon ya koma wani haɗari tare da canja fasaha d dabarun kai hare-hare. Hakan ya biyo bayan harba jiragen mara matuki daga Kudancin Lebanon da yin nasarar shiga mai zurfi a cikin Isra'ila, sun haifar da barna ga sojojin Isra'ila a wani samame na baya-bayan nan. Asarar da aka yi ta tabbatar da cewa Hizbullah ba kawai da ƙarfin makamai masu linzami ta dogara ba ne, sai dai ma a lokaci guda kuma tana da ikon keta sararin samaniya da tattara bayanan sirri, da key a na iya fuskanta da kai hari katsaye rukunan tsaron Isra'ila.

Kwararru na soji suna fassara wannan canjin dabarun jiragen marasa matuki na Hizbullah a matsayin "inganta yaki maras daidaito". An bayyana cewa ƙungiyar tana amfani da jiragen mara matuka masu dogon zango, masu wuyar ganowa, da takamaiman salon kai hari kamar "garken ƙudan zuma". Wannan yana ƙara matsin lamba a kan wuraren sa ido na Isra'ila da sansanonin soji a kan iyaka har ya kai matsayin da Isra’ila ba zata iya jurewa ba. An bayyana cewa tasirin yawaitar hare-haren jiragen marasa matuki a kan tsarin tsaron saman Isra'ila wato "Kubbar ƙarfe" da sauran tsarin na’urori masu haɗaka, yana jinkirta yiwuwar mai da martanin tsaro.

A bangaren Isra'ila, waɗannan hare-haren sun tayar da muhawara a cikin gida game da nasarar dabarun soji a fagen arewa. Majiyoyin soji sun yi ikrarin cewa dakatar da barazanar jiragen marasa matuki gaba daya yana da matukar hadarin mai cike da kuskure da yanayin ƙasa baya bayar ikon da hakan. Faruwar asara ya haifar da alamar tambaya a cikin al'ummar Isra'ila game da dorewar kasancewar soji a yankin da kuma ko ƙarfin rage hare-haren.

Wannan ƙarin matsin lamba na Hizbullah a fagen, ya zama wani muhimmin batu mai nuna yadda ko a cikin ƙaramin fagen fama, fifikon fasaha zai iya dagula ma'auni. Alamu da ke nuna cewa ƙungiyar ta inganta runbun jiragen marasa matukin ta da duka a adadi mai inganci, wanda ke ƙara gargadi game da hadarin "makantar tsaron sama" da Isra'ila za ta iya fuskanta a yanayin wani babban rikici.

………………………………………………………………..

Your Comment

You are replying to: .
captcha